Genesis 38:12 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Bayan an daɗe sai matar Yahuda, ’yar Shuwa ta rasu. Sa’ad da Yahuda ya gama makoki, sai ya haura zuwa Timna, zuwa wurin mutanen da suke askin tumakinsa, abokinsa Hira mutumin Adullam kuwa ya tafi tare da shi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَنَانً، یَرْ شُوحُ مَاتَرْ يَهُودَ تَمُتُ؞ بَايَنْدَ ݣُونَكِنْ كُوكَنْ مُتُوَرْتَ سُكَ وُثٜىٰ، سَيْ يَهُودَ دَ أَبُواْكِنْسَ حِرَ مُتُمِنْ أَدُلَّمْ سُكَ هَوْرَ ذُوَا غَرِنْ تِمْنَ وُرِنْ دَ مَاسُ أَسْكِنْ غَاشِنْ تُمَكِنْسَ سُكٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A kwana a tashi, ga matar Yahuza, 'yar Shuwa ta rasu. Da Yahuza ya gama karɓar ta'aziyya, sai ya haura Timna wurin masu sausayar tumakinsa, da shi da abokinsa Hira Ba'adullame.