Genesis 38:18 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya ce, “Wace jingina zan ba ki?” Sai ta amsa, “Hatiminka da ka rataye a wuya da kuma sandan da yake a hannunka.” Ya ba da su gare ta, ya kuma kwana da ita, sai ta yi ciki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَأَمْسَ «وَثٜىٰ إِرِنْ شَيْدَثٜىٰ ذَنْبَاكِ؟» سَيْ تَثٜىٰ «هَاتِمِنْكَ وَنْدَ يَنَ أَ رَاتَيٜىٰ أَوُيَنْكَ دَ كُمَ سَنْدَنْ تَڢِيَرْكَ؞» دُواْمِنْ حَكَ يَبَاتَسُ، سَيْ يَشِغَ يَݣُونَ دَ عِتَ، تَا كُوَ طَوْكِ ثِكِنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya ce, “Wane alkawari zan yi miki?” Ta amsa, ta ce, “Ba ni hatiminka da ɗamararka da sandan da yake a hannunka.” Ya kuwa ba ta su, ya kwana da ita. Sai ta yi ciki.