Genesis 38:25 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yayinda ake fitar da ita, sai ta aika saƙo zuwa wurin surukinta, ta ce, “Mutumin da yake da waɗannan kayan ne ya yi mini ciki.” Ta kuma ƙara da cewa, “Duba ko za ka gane da hatimin nan, da abin ɗamaran nan, da kuma sandan nan, ko na wane ne?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَدَّ عَكٜىٰ ڢِتَرْدَ عِتَ، سَيْ تَعَيْكَ دَ سَڧُواْ وَ بَابَنْ مِجِنْتَ تَثٜىٰ «مُتُمِنْ دَ يَكٜىٰدَ كَايَنَّنْ نٜىٰ يَيِ مِنِ ثِكِ؞ دُوبَ كُواْ ذَاكَ غَانٜىٰ هَاتِمِ دَ إِغِيَرْسَ دَ كُمَ سَنْدَنْ تَڢِيَرْ نَنْ، كُواْ نَوَنٜىٰنٜىٰ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Za a fito da ita ke nan sai ta aika wa surukinta, ta ce, “Wanda yake da waɗannan kaya shi ya yi mini ciki.” Ta kuma ce, “Ka shaida, ina roƙonka, ko na wane ne wannan hatimi, da abin ɗamarar, da sanda.”