Genesis 42:13 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne, ’yan’uwa, ’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ سُكَثٜىٰ «رَنْكَيَدَطٜىٰ، مُو بَايِنْكَ یَنْعُوَ نٜىٰ غُواْمَشَا بِيُ، كُمَ یَیَنْ مُتُمْ غُدَا عَڧَسَرْ كَنْعَنَ؞ أَوْتَنْمُ يَنَ تَرٜىٰدَ بَابَنْمُ، طَيَنْمُ كُمَ بَاشِ دَ رَيْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Suka ce, “Mu bayinka, 'yan'uwan juna ne, mu goma sha biyu muke maza, 'ya'yan mutum guda a ƙasar Kan'ana, ga shi kuwa autanmu yana tare da mahaifinmu a yanzu, ɗayan kuwa ya rasu.”