Genesis 42:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Nan da nan da Yusuf ya ga ’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ يُوسُڢَ يَغَ یَنْعُوَنْسَ سَيْ يَغَانٜىٰ دَسُو، عَمَّا يَا مَيْدَسُو كَمَرْ بَاڧِ، يَيِ مُسُ مَغَنَ دَ ذَاڢِ؞ يَثٜىٰ مُسُ «دَغَ إِنَا كُكَ ڢِتُواْ؟» سُكَثٜىٰ «دَغَ ڧَسَرْ كَنْعَنَ دُواْمِنْ مُسَيِ عَبِنْثِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Da Yusufu ya ga 'yan'uwansa, ya gane da su, amma ya mai da su kamar baƙi, ya yi musu magana da gautsi ya ce, “Daga ina kuka fito?” Suka ce, “Daga ƙasar Kan'ana muka zo sayen abinci.”