Genesis 43:29 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Da ya ɗaga idanu, sai ya ga ɗan’uwansa Benyamin, ɗan mahaifiyarsa, sai ya yi tambaya, “Wannan ne ƙaramin ɗan’uwanku, wanda kuka faɗa mini a kai?” Ya kuma ce, “Allah yă yi maka albarka, ɗana.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يُوسُڢَ يَا دُوبَ يَغَ طَنْعُوَنْسَ بِلِيَامِنُ، طَنْ دَ مَامَرْسَ تَحَيْڢَ، يَثٜىٰ «وَنَّنْ شِينٜىٰ أَوْتَنْكُ، وَنْدَ كُكَيِ مِنِ مَغَنَ عَكَنْسَ؟ اللَّهْ يَيِ مَكَ أَلْحٜىٰرِ، طَانَ!»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai ya ɗaga idanunsa, ya ga ɗan'uwansa Biliyaminu, ɗan da mahaifiyarsa ta haifa, ya ce, “Wannan shi ne auta naku, wanda kuka yi mini magana a kansa? Allah ya yi maka alheri ɗana!”