Genesis 44:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yahuda ya amsa ya ce, “Me za mu ce wa ranka yă daɗe? Yaya kuma za mu wanke kanmu daga wannan zargi? Allah ya tona laifin bayinka. Ga mu, za mu zama bayinka, da mu da wanda aka sami kwaf ɗin a hannunsa.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ يَهُودَ يَثٜىٰ «رَنْكَيَدَطٜىٰ! مٜىٰ ذَامُثٜىٰ؟ وَثٜىٰ مَغَنَ ذَامُيِ؟ كُواْ كُوَ تَيَيَا ذَامُ وَنْكٜىٰ كَنْمُ؟ يَا شُوغَبَنَ، اللَّهْ نٜىٰ يَتُواْنَ لَيْڢِنْ بَايِنْكَ؞ غَا مُو، مُو بَايِنْكَ نٜىٰ دَمُو دَ وَنْدَ عَكَ سَامِ ݣُوڢْ طِنْ أَ حَنُّنْسَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sai Yahuza ya amsa, “Me za mu ce wa shugabana? Wace magana za mu yi? Ko kuwa, ta yaya za mu baratar da kanmu? Allah ne ya tona laifin bayinka, ga mu, mu bayin shugabana ne, da mu da shi wanda aka sami finjalin a wurinsa.”