Genesis 47:1 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da ’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً يُوسُڢَ يَذُواْ يَڢَطَا وَ ڢِرْعَوْنَ يَثٜىٰ «بَابَنَ دَ یَنْعُوَنَ دَ غَرْكُنَنْسُ نَأَوَكِ دَ تُمَكِ دَ نَشَانُو دَ دُكَنْ أَبِنْدَ سُكٜىٰ دَشِ، سُنْ ذُواْ دَغَ ڧَسَرْ كَنْعَنَ، يَنْذُ سُنَ عَيَنْكِنْ غُواْشٜىٰنْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yusufu ya shiga ya yi magana da Fir'auna, ya ce, “Mahaifina da 'yan'uwana, da garkunansu na awaki da na tumaki, da garkunan shanu, da dukan abin da suka mallaka, sun zo daga ƙasar Kan'ana, yanzu suna ƙasar Goshen.”