Genesis 48:4 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
ya kuma ce mini, ‘Zan sa ka yi ta haihuwa ka kuma riɓaɓɓanya, za ka ƙaru a yawa. Zan mai da kai al’ummar mutane, zan kuma ba ka wannan ƙasa tă zama madawwamiyar mallaka ga zuriyarka a bayanka.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَثٜىٰ مِنِ، ‹غَاشِ، ذَنْسَا كَيَلْوَتَ كَيِ تَحَيْڢُوَ سُواْسَيْ؞ ذَنْ كُمَسَا ذُرِيَرْكَ تَذَمَ تَارُوانْ ڧَبِيلُ، إِنْ بَادَ ڧَسَرْ نَنْ غَرٜىٰسُ تَذَمَ غَادُوانْسُ حَرْ أَبَدَا؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ya ce mini, ‘Ga shi, zan sa ka hayayyafa, in riɓaɓɓanya ka, zan maishe ka ƙungiyar al'ummai, zan kuwa ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka ta zama madawwamiyar mallaka.’