Genesis 48:5 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“To, yanzu, ’ya’ya mazanka biyu da aka haifa maka a Masar kafin in zo a nan za su zama nawa; Efraim da Manasse za su zama nawa, kamar yadda Ruben da Simeyon suke nawa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«يَنْذُ دُكْ یَیَنْكَ بِيُ مَظَا وَطَنْدَ عَكَ حَيْڢَ مَكَ عَڧَسَرْ مَصَرْ كَاڢِنْ ذُوَانَ وُرِنْكَ، سُو طِنْ نَوَنٜىٰ؞ إِڢْرَيِمْ دَ مَنَسّٜىٰ ذَاسُ ذَمَ نَوَ، كَمَرْ يَدَّ رَعُبَيْنُ دَ سِمٜىٰيُوانْ سُكٜىٰ نَوَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yanzu fa, a kan waɗannan 'ya'yanka maza biyu da aka haifa a Masar kafin zuwana, su nawa ne, Ifraimu da Manassa za su zama nawa, kamar yadda su Ra'ubainu da Saminu suke.