Genesis 50:17 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da za ku ce wa Yusuf, ‘Na roƙe ka, ka gafarta wa ’yan’uwanka zunubai da laifofin da suka aikata na abubuwa marasa kyau da suka yi maka.’ Yanzu muna roƙonka ka gafarta zunuban bayin Allah na mahaifinka.” Sa’ad da saƙonsu ya zo masa, sai Yusuf ya yi kuka.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُثٜىٰمَكَ يَنَ ضُواْڧُوانْكَ، كَغَاڢَرْتَا وَیَنْعُوَنْكَ مُغُنْتَادَ لَيْڢِنْدَ سُكَيِ مَكَ، يَدَّ دَا سُكَ بَاكَ وَهَلَ؞ سَبُواْدَ حَكَ مُنَ ضُواْڧُوانْكَ كَغَاڢَرْثٜىٰمُ، مُو بَايِنْ اللَّهْ نَبَابَنْكَ؞» يُوسُڢَ كُوَ يَيِ كُوكَا سَعَدَّ سُكَيِ وَنَّنْ مَغَنَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
ya ce, ‘Ku faɗa wa Yusufu, ina roƙonsa, ya gafarta laifin 'yan'uwansa da zunubansu, gama sun yi masa mugunta.’ Yanzu fa, muna roƙonka, ka gafarta laifofin bayin Allah na mahaifinka.” Yusufu ya yi kuka sa'ad da suka yi magana da shi.