Habakkuk 2:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “ ‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُكَنْ ڧَبِيلُنَّنْ ذَاسُيِ غَابَادَشِ، سُنَ مَسَ دَارِيَا دَ رٜىٰنِ ثٜىٰوَ «كَيْتُوانْكَ، مَيْ تَتَّارَ أَبِنْدَ بَنَكَبَ! حَرْ يَوْشٜىٰ، ذَاكَ تَارَ وَكَنْكَ أَرْزِڧِ تَوُرِنْ عَيْكِنْ ثُوتَا؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ai, waɗannan duka za su yi ta yi masa zambo, Su yi masa dariya ta raini, Su ce, ‘Tasa ta ƙare, shi wanda ya tattara abin da ba nasa ba, Har yaushe zai riƙa arzuta kansa ta hanyar ba da rance?’