Habakkuk 3:16 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Na ji sai zuciyata ta buga, leɓunana sun yi rawa da jin murya; ƙasusuwana suka ruɓe, ƙafafuna kuma sun yi rawa. Duk da haka zan jira da haƙuri ga ranar bala’i ta zo a kan al’umman nan mai kawo mana hari.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَنَجِ، سَيْ جِكِينَ يَيِ ضَوَ، لٜىٰٻُنَ سُكَيِ ضَوَ دَ ڟُواْرُواْ؞ غَٻُواْٻِنْ جِكِينَ سُكَ مُتُ، إِنَ تَڢِيَ ڧَڢَاڢُنَ سُنَ ضَوَ؞ دُكْدَهَكَ، ذَنْيِ شِضُ إِنَ جِرَا رَانَرْ عَذَابَ، عَذَابَرْ دَ ذَاتَ ڢَاطُواْ عَكَنْ مُتَنٜىٰنْ دَسُكٜىٰ كَٰوُاْ مَنَ يَاڧِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da na ji, sai jikina ya yi rawa, Leɓunana suka raurawa. Ƙasusuwana suka ruɓe, sai na yi rawar jiki. Zan yi shiru in jira ranar wahala da za ta zo A kan waɗanda suka kawo mana yaƙi.