Haggai 2:22 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan hamɓarar da gadajen mulki in kuma ragargaza ƙarfin ƙasashen al’ummai. Zan tumɓuke kekunan yaƙi da mahayansu; dawakai da mahayansu za su mutu, kowane ta wurin takobin ɗan’uwansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْ كُمَ تُمْٻُكٜىٰ مُلْكٍ ڧَسَاشٜىٰ؞ إِنَ سُواْ إِنْ كَرْيَ ڧَرْڢِنْ مُلْكٍ ڧَسَاشٜىٰنْ أَلْعُمَّيْ، ذَنْ كُمَ تُمْٻُكٜىٰ كٜىٰكُنَنْ دُواْكِ دَ مَاسُ هَوَنْسُ؞ دَوَكِ ذَاسُ ڢَاطِ، مَاسُ هَوَنْسُ كُمَ ذَاسُ كَكَّشٜىٰ جُونَ دَ تَكُبَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zan kuma hamɓare gadon sarautan daula, in kuma karya ƙarfin daular al'umman. Zan kuma hallaka karusai da mahayansu. Sojojin dawakai kuma za su kashe junansu da takuba.