Hosea 1:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Duk da haka Isra’ilawa za su zama kamar yashi a bakin teku, da ba za a iya aunawa ko a ƙirga ba. A inda aka ce musu, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ za a kira su ‘’ya’yan Allah mai rai.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُكْدَهَكَ يَوَنْ ذُرِيَرْ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَيْ كَسَنْثٜىٰ كَمَرْ يَشِ عَبَاكِنْ تٜىٰكُ، وَنْدَ بَعَ عِيَ عَوْنَاوَا كُواْ ڧِرْغَوَ؞ عِنْدَ كُمَ دَا عَكَثٜىٰ مُكُ «كَا بَمُتَنٜىٰنَ بَنٜىٰ،» ذَاعَ ثٜىٰ دَكُو «یَیَنْ اللَّهْ مَيْ رَيْ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Duk da haka yawan mutanen Isra'ila Zai zama kamar yashi a bakin teku, Wanda ba za a iya aunawa ko ƙidayawa ba. Maimakon kuma a ce, ‘Ku ba mutanena ba ne,’ Za a ce, ‘Ku mutanen Allah ne mai rai.’