Hosea 8:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Isra’ila ya manta da Mahaliccinsa ya kuma gina fadodi; Yahuda ya gina katanga a yawancin garuruwansa. Amma zan aiko da wuta a bisa biranensu da zai cinye kagaransu.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِسْرَٰٓءِيلَ سُنْ مَنْتَادَ وَنْدَ يَحَلِثّٜىٰسُ؞ سُنْ غِنَا مَنْيَنْ غِدَاجٜىٰنْ سَرْكِے؞ يَهُودَ مَا تَغِنَ بِرَنٜىٰنْ كَتَنْغَ مَاسُيَوَ؞ عَمَّا ذَنْ عَيْكَ دَ وُتَا عَكَنْ بِرَنٜىٰنْ، وُتَرْ ذَاتَ ثِنْيٜىٰ غِدَاجٜىٰنْ سَرَاكُنَنْسُ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Gama mutanen Isra'ila sun manta da Mahaliccinsu, Sai sun gina manyan gidaje masu daraja. Mutanen Yahuza kuma sun yawaita biranensu masu garu, Amma ni Ubangiji, zan aika da wuta a kan biranensu, Ta ƙone fādodinsu.”