Isaiah 10:20 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ رَانَرْ نَنْ ضَغُواْوَرْ مُتَنٜىٰنْ إِسْرَٰٓءِيلَ، مَاسُ ڟِيرَا نَغِدَنْ يَعْڧُوبَ، بَذَاسُ ڧَارَ دُواْغَضَ غَ مَاسُ هَلَّكَسُبَ، ذَاسُ دُواْغَضَ طُنْ‌غُمْ غَ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ڟَرْكِے نَ إِسْرَٰٓءِيلَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Lokaci zai yi sa'ad da jama'ar Isra'ila da suka ragu ba za su ƙara dogara ga al'ummar da ta kusa hallaka su ba. Hakika za su dogara ga Ubangiji Allah, Mai Tsarki na Isra'ila.