Isaiah 14:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ڧَبِيلُ دَيَوَ ذَاسُ تَيْمَكِ إِسْرَٰٓءِيلَاوَا سُكُواْمَ ڧَسَرْسُ؞ غِدَنْ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَاسُسَا ڧَبِيلُنْ سُيِ مُسُ بَوْتَا عَڧَسَرْ يَهْوٜىٰهْ ؞ إِسْرَٰٓءِيلَ ذَاتَ مَيْدَ وَطَنْدَ دَا سُكَ مَلَّكٜىٰسُ بَايِ، ذَاسُيِ مُلْكِ عَكَنْ وَطَنْدَ دَا سُكَيِ مُسُ دَنِّيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Al'ummai da yawa za su taimaki jama'ar Isra'ila su koma ƙasarsu wadda Ubangiji ya ba su. A can sauran al'umma za su yi wa Isra'ila hidima kamar bayi. Waɗanda suka kama Isra'ilawa a dā yanzu Isra'ilawa za su kama su. Jama'ar Isra'ila za ta mallaki waɗanda suka taɓa zaluntarsu.