Isaiah 16:14 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma yanzu Ubangiji ya ce, “Cikin shekara uku, kamar yadda bawan da aka bautar da shi bisa ga yarjejjeniya zai lissafta, haka za a mai da daraja da kuma dukan yawan mutanen Mowab abin reni, daga ɗumbun mutanenta, ’yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَمَّا يَنْذُ يَهْوٜىٰهْ يَنَ ثٜىٰوَ «عَثِكِنْ شٜىٰكَرَا عُكُ بِسَغَ لِسَّڢِ نَشٜىٰكَرُ نَمَيْ عَيْكِنْ لٜىٰبُرَ، طَوْكَكَرْ مُواْوَبْ ذَاتَ ڢَاطِ، دُكْ دَ يَوَنْ جَمَعَرْتَ؞ مُتَنٜىٰنْتَ كُوَ دَ سُكَ رَغُ ذَاسُ كَسَنْثٜىٰ كَطَنْ كَوَيْ، ذَاسُ كُمَ ذَمَ مَرَسَ ڧَرْڢِے؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yanzu Ubangiji ya ce, “A shekara uku daidai, dukiyar Mowab mai yawan nan za ta ƙare. Daga cikin ɗumbun mutanenta 'yan kaɗan ne kaɗai za su ragu, za su kuma zama marasa ƙarfi.”