Isaiah 16:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gonakin Heshbon sun bushe, inabin Sibma ma haka. Masu mulkin al’ummai sun tattake inabi mafi kyau, waɗanda suka taɓa yaɗuwa zuwa Yazer suka bazu ta wajen hamada. Tohonsu sun buɗu suka kai har teku.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمَا غُواْنَكِنْ هٜىٰشْبُوانْ سُنْ يَنْڨُونٜىٰ، غُواْنَكِنْ إِنَبِے نَ سِبْمَ سُنْ بُوشٜىٰ، غُواْنَكِنْ دَ دَا ضُوً إِنَبِنْسُ يَكٜىٰسَا مَاسُ مُلْكٍ أَلْعُمَّيْ سُبُغُ؞ دَا مُواْوَبْ كَمَرْ إِتَاثٜىٰنْ إِنَبِنٜىٰ وَنْدَ يَبَظُو ذُوَا يَظٜىٰرْ حَرْ ثِكِنْ هَمَادَ، وَنْدَ سَيْوُاْيِنْسَ سُنْ مِيڧٜىٰ حَرْ ڧٜىٰتَرٜىٰنْ تٜىٰكُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Gonakin da suke kusa da Heshbon, da gonakin inabin da suke Sibma an lalatar da su, gonakin inabin nan waɗanda ruwan inabinsu suke sa masu mulkin al'ummai su bugu. Da kurangunsu sun taɓa yaɗuwa zuwa gabas har suka kai birnin Yazar da cikin hamada, wajen yamma kuma sai da suka dangana da gefen Tekun Gishiri.