Isaiah 2:19 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Mutane za su gudu zuwa kogwannin duwatsu da kuma ramummuka a ƙasa daga razanar Ubangiji da kuma darajar ɗaukakarsa, sa’ad da ya tashi don yă girgiza duniya.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مُتَنٜىٰ ذَاسُ شِغَ كُواْڠُونِّنْ دُوَڟُو سُشِغَ رَامُكَنْ ڧَسَا، سُغُدُ دَغَ ڢُشِنْ يَهْوٜىٰهْ ، دَغَ كُمَ طَوْكَكَرْ دَرَجَرْسَ، سَعَدَّ يَتَاشِ يَڟُواْرَتَرْ دَ دُونِيَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutane za su ɓuya a kogwannin duwatsu, ko su haƙa ramummuka a ƙasa, suna ƙoƙarin tserewa daga fushin Ubangiji, ko su ɓuya daga ikonsa da ɗaukakarsa, sa'ad da ya zo domin ya girgiza duniya.