Isaiah 20:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
a wannan lokaci Ubangiji ya yi magana ta wurin Ishaya ɗan Amoz. Ya ce masa, “Tuɓe tsummokin da kake saye da su, da kuma takalman da ka sa a ƙafafu.” Ya kuwa yi haka, yana yawo tsirara kuma ba takalma a ƙafa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ شٜىٰكَرَرْ نَنْ يَهْوٜىٰهْ يَايِ مَغَنَ دَ عِشَايَ طَنْ أَمُواظْ ثٜىٰوَ «تَڢِے كَتُوٻٜىٰ رِيغُنَنْكَ نَنُونَ بَڧِنْ ثِكِ دَغَ جِكِنْكَ، كَكُمَ ثِرٜىٰ تَاكَلْمَنْكَ دَغَ ڧَڢَاڢُنْكَ؞» عِشَايَ يَكُوَ يِهَكَ، يَيِ تَتَڢِيَ ڟِرَرَ بَابُ تَاكَلْمَ عَڧَڢَاڢُنْسَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A wannan lokaci Ubangiji ya riga ya faɗa wa Ishaya ɗan Amoz, cewa ya tuɓe tsummokin da yake saye da su, ya kuma tuɓe takalmansa. Shi kuwa ya yi biyayya ya yi ta yawo tsirara, ba kuma takalmi a ƙafarsa.