Isaiah 21:9 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Duba, ga wani mutum tafe a keken yaƙin tare da ƙungiyar dawakai. Ya kuma mayar da amsa, ‘Babilon ta fāɗi, ta fāɗi! Dukan siffofin allolinta kwance a ragargaje a ƙasa!’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دُوبَ، غَ كٜىٰكُنَنْ دُواْكِ سُنَ ذُوَا بِيُ بِيُ، غَ سُواْجُواْجِ مَاسُ هَوَنْ دُواْكِ سُنَ ذُوَا!» سَيْ طَنْ سِنْتِرِنْ يَثِيغَبَدَ ثٜىٰوَ «بَابِيلَ تَڢَاطِ، عِ، تَڢَاطِ! دُكَنْ صِڢُّواْڢِنْ أَلُّواْلِنْتَ، أَنْڢَرْڢَشٜىٰسُ غَبَاطَيَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Farat ɗaya sai ga su sun zo! Suna tafe a kan dawakai biyu biyu. Sai mai tsaro ya ba da labari cewa, “Babila ta fāɗi! Dukan gumakan da suke yi wa sujada an ragargaza su har ƙasa.”