Isaiah 22:25 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ رَانَرْ نَنْ، ڧُوسَرْ دَ عَكَ كَڢَ أَوُرِے مَيْ ڧَرْڢِے ذَاتَ كَرْيٜىٰ تَڢَاطِ ڧَسَا؞ دُكَنْ أَبِنْدَ يَكٜىٰ أَ رَاتَيٜىٰ كُوَ ذَيْ هَلَّكَ؞» غَمَا يَهْوٜىٰهْ نٜىٰ يَڢَطَا؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'ad da wannan ya faru ragayar da aka ɗaura tam za ta tsinke ta fāɗo. Wannan shi ne ƙarshen kowane abin da aka sa a cikin ragayar ke nan. Ni Ubangiji Mai Runduna na faɗa.”