Isaiah 25:1 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا يَهْوٜىٰهْ ، كَيْنٜىٰ اللَّهْ نَا، ذَنْ طَوْكَكَاكَ، إِنْ يَبِے سُونَنْكَ؞ غَمَا كَايِ أَيُّكَنْ بَنْ مَامَاكِ، تُنْ تُنِ كَيِ نُڢِنْسُ ثِكِنْ أَمِنْثِ دَ غَسْكِيَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya Ubangiji, kai ne Allahna, Zan ɗaukaka ka, in yabi sunanka. Ka aikata al'amura masu banmamaki, Ka tafiyar da su da aminci, Wato bisa ga shirin da ka yi tuntuni.