Isaiah 26:11 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا يَهْوٜىٰهْ ، حَنُّنْكَ يَنَ مِيڧٜىٰ أَ سَمَ، عَمَّا بَسُ غَنِبَ؞ بَرِ كَسَا سُغَ ڨُوظُوانْكَ غَ جَمَعَرْكَ، سُجِ كُنْيَا؞ بَرِ وُتَرْ دَ عَكَ شِرْيَ وَمَاسُ ڧِنْكَ تَثِنْيٜىٰسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Maƙiyanka ba su san za ka hukunta su ba. Ya Ubangiji, ka kunyatar da su, ka sa su sha wahala, Wato su sha wahalar hukuncin da ka shirya. Ka nuna musu yawan ƙaunar da kake yi wa jama'arka.