Isaiah 26:19 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، «مُتَنٜىٰنْكُ دَ سُكَ مُتُ ذَاسُ رَايُ، غَوَوَّكِنْسُ ذَاسُ تَاشِ! يَا كُو مَاسُ ذَمَ عَڧُورَا، كُتَاشِ كُيِ وَاڧُواْڧِنْ ڢَضٍ ثِكِ! يَدَّ رَٻَ تَكَنْ سَابُنْتَا ڢُسْكَرْ ڧَسَا، حَكَ، نِے يَهْوٜىٰهْ ذَنْ رَايَرْ دَ وَطَنْدَ سُكَ مُتُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Mutanenmu da suka mutu za su sāke rayuwa! Jikunansu za su sāke rayuwa! Dukan waɗanda suke kwance cikin kaburburansu Za su farka, su yi waƙa don farin ciki! Kamar laimar raɓa wanda yake wartsakar da duniya, Haka Ubangiji zai rayar da waɗanda suka daɗe da mutuwa.