Isaiah 27:11 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’ad da rassanta suka bushe, sai su kakkarye su mata kuma su zo su yi itacen wuta da su. Gama mutane ne marar azanci; saboda haka Mahaliccinsu bai ji tausayinsu ba, Mahaliccinsu bai nuna musu jinƙai ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
دَ رَسَّنْ عِتَتُوَ سُكَ بُوشٜىٰ، سُنْ كَرْيٜىٰ، مَاتَا سُكَ ݣُوشٜىٰ دُواْمِنْ سُهُورَ وُتَادَسُو؞ سَبُواْدَ سُو مُتَنٜىٰنٜىٰ دَ بَاسُ دَ غَانٜىٰوَ، شِے وَنْدَ يَيِسُ بَذَيْجِ تَوْسَيِنْسُبَ، شِے وَنْدَ يَحَلِثّٜىٰسُ بَذَيْ نُونَ مُسُ جِنْڧَيْبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Rassan itatuwa sun bushe sun kakkarye, mata kuwa sun tattara, don su riƙa hura wuta da su. Da yake jama'a ba su gane kome ba, Allah Mahaliccinsu ba zai ji tausayinsu ba, ba zai nuna musu jinƙai ba.