Isaiah 27:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kuma a wannan rana zai busa ƙaho mai kāra sosai. Waɗanda suke mutuwa a Assuriya da kuma waɗanda aka kai zaman bauta a Masar za su zo su kuma yi wa Ubangiji sujada a dutse mai tsarki a Urushalima.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
أَ رَانَرْ نَنْ، ذَاعَ بُوسَ ڧَهُواْ دُواْمِنْ عَكِرَوُاْ إِسْرَٰٓءِيلَاوَنْ دَ سُكَ ٻَثٜىٰ ثِكِنْ ڧَسَرْ أَسُّرِيَ دَ وَطَنْدَ عَكَ كُواْرَ ذُوَا ڧَسَرْ مَصَرْ، سُذُواْ سُيِ سُجَّدَ غَ يَهْوٜىٰهْ عَتُدُنْسَ مَيْ ڟَرْكِے أَ عُرُوشَلِيمَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A wannan rana za a busa ƙaho don a kirawo Isra'ilawan da suke zaman baƙunci a Assuriya da Masar. Za su zo su yi wa Ubangiji sujada a Urushalima a tsattsarkan dutsensa.