Isaiah 28:16 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce, “Duba, na kafa dutse a Sihiyona, dutsen da aka gwada, dutsen kusurwa mai daraja don tabbataccen tushe; wanda ya dogara gare shi ba zai taɓa shan kunya ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَنْذُ ڢَا إِنْجِ عُبَنْ‌غِجِ يَهْوٜىٰهْ ، «غَاشِ، إِنَ كَڢَ دُوڟٜىٰ أَ سِهِيُواْنَ، دُوڟٜىٰنْ دَ عَكَ ڠُودَ عَكَ تَبَّتَرْ، دُوڟٜىٰ مَيْ دَرَجَ مَڢِے أَمْڢَانِ أَغِنِ، تَبَّتَاثّٜىٰنْ تُوشٜىٰ، ‹دُكْ مَيْ أَمِنْثٜىٰ دَشِ، بَذَيْ ڢِرْغِتَبَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Yanzu fa ga abin da Ubangiji ya ce, “Zan kafa ƙaƙƙarfan harsashin gini a Sihiyona. A kansa zan sa ƙaƙƙarfan dutsen kusurwa. A kansa an rubuta wannan magana, ‘Amincin da yake kafaffe mai haƙuri ne kuma.’