Isaiah 29:13 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun zo kusa da ni da bakinsu suka kuma girmama ni da leɓunansu, amma zukatansu suna nesa daga gare ni. Sujadar da suke mini cike take da dokokin da mutane suka koyar.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عُبَنْغِجِ يَثٜىٰ، «مُتَنٜىٰنَّنْ ڢَا، دَ بَاكِ كَوَيْ سُكٜىٰيِ مِنِ سُجَّدَ، دَ مَغَنَ كَوَيْ سُكٜىٰ غِرْمَمَ نِے، عَمَّا ذُوثِيَارْسُ سُنَ نٜىٰسَ دَنِے، سُجَّدَرْسُ بَا وَنِ أَبُ بَنٜىٰ، سَيْ عُمَرْنَيْ نٜىٰ دَسُكَ هَدَّثٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce, “Waɗannan mutane sun ce suna mini sujada, amma kalmominsu ba su da ma'ana, zukatansu kuma suna wani wuri dabam. Addininsu ba wani abu ba ne, sai dai dokoki ne da ka'idodin mutane da suka haddace.