Isaiah 29:7 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Sa’an nan sojojin dukan al’umman da suka yi yaƙi da Ariyel, da suka fāɗa mata da kagararta suka kuma yi mata kwanto, za su zama kamar yadda yake da mafarki, wahayi da dare,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَعَنً دُكَنْ يَوَنْ أَلْعُمَّنْ دَسُكٜىٰ يَاڧِ دَ أَرِيٜىٰلْ بَغَدٜىٰنْ اللَّهْ ، دُكْ مَاسُ يَاڧِنْتَ، دُكْ مَاسُ رُشٜىٰ كَتَنْ‌غَرْتَ، دَ مَاسُ بَاتَ عَذَابَ، دُكَنْسُ ذَاسُ ٻَثٜىٰ كَمَرْ مَڢَرْكِ، كَمَرْ غَنِنْ رُعُيَ دَدَرٜىٰ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan dukan sojojin sauran al'umman da suka fāɗa wa birni inda bagaden Allah yake da yaƙi, da dukan makamansu, da kayayyakin yaƙinsu, kome da kome za su shuɗe kamar mafarki, kamar tunanin dare.