Isaiah 31:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kaiton waɗanda suka gangara zuwa Masar don neman taimako, waɗanda suke dogara ga dawakai, waɗanda suke dogara ga yawan kekunan yaƙinsu da kuma a girman ƙarfin mahayan dawakansu, amma ba sa dogara ga Mai Tsarkin nan na Isra’ila, ko ya nemi taimako daga Ubangiji.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَيْتُواْ! كُنَ غَنْغَرَوَ ذُوَا مَصَرْ دُواْمِنْ نٜىٰمَنْ تَيْمَكُواْ، كُنَ دُواْغَضَ غَ دَوَكِ، كُنَ دُواْغَضَ غَ يَوَنْ كٜىٰكُنَنْ دُواْكِنْ يَاڧِ، كُنَ دُواْغَضَ غَ ڧَرْڢِنْ مَاسُ هَوَنْ دُواْكِ، عَمَّا بَكُ دُواْغَضَ غَ مَيْ ڟَرْكِے نَ إِسْرَٰٓءِيلَ، كُواْ كُنٜىٰمِ شَوَرَا دَغَ وُرِنْ يَهْوٜىٰهْ بَ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Waɗanda suka tafi Masar neman taimako, sun shiga uku! Suna dogara ga ƙarfin tulin dawakan Masar na yaƙi, da karusansu, da sojojinsu. Amma ba su dogara ga Ubangiji, Allah Mai Tsarki na Isra'ila ba, ba su ko roƙe shi taimako ba.