Isaiah 32:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Za a ƙyale kagarar, a gudu a bar birnin da dā ake hayaniya; mafaka da hasumiyar tsaro za su zama kango har abada, jin daɗin jakuna, makiyaya don garkuna,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
غَمَا ذَاعَ ڨَلٜىٰ غِدَنْ سَرْكِے، بِرْنِ مَيْ يَوَنْ مُتَنٜىٰ كُمَ ذَاعَ بَرْ شِ بَا كُواْوَ؞ تُدُ دَ طَاكِنْ طَنْ سِنْتِرِ ذَاسُ ذَمَ كُواْغُوانْ كَرٜىٰنْ دَاجِ؞ ذَاسُ ذَمَ وُرِنْ وَسَ دُواْمِنْ جَاكِنْ دَاجِ، دَ وُرِنْ كِيوُاْ دُواْمِنْ تُمَكِ،
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Har ma za a bar fādar, babban birnin sarauta kuma za a gudu a bar shi gaba ɗaya. Gidaje kuma da kagaran da take tsaronsu za su zama rusassu har abada. A can jakunan jeji za su yi ta zarya, tumaki kuma za su sami wurin kiwo.