Isaiah 33:14 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Masu zunubi a Sihiyona sun firgita; rawar jiki ya kama marasa sanin Allah suna cewa, “Wane ne a cikinmu zai iya zama da wuta mai ci? Wane ne a cikinmu zai iya zama da madawwamiyar ƙonewa?”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
مَاسُ ذُنُوبِ أَ سِهِيُواْنَ سُنَ جِنْ ڟُواْرُواْ؞ ضَوَرْ جِكِے تَكَامَ مَرَسَ ڟُواْرُوانْ اللَّهْ ؞ سُنَ ثٜىٰوَ «وَنٜىٰنٜىٰ دَغَ ثِكِنْمُ ذَيْ عِيَ ذَمَ دَ وُتَا مَيْ ثِنْيٜىٰوَ؟ وَنٜىٰنٜىٰ دَغَ ثِكِنْمُ ذَيْ عِيَ ذَمَ دَ وُتَا مَرَرْ مُتُوَ؟»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Jama'ar Sihiyona cike da zunubi suke, suna ta rawar jiki don tsoro. Suka ce, “Hukuncin Allah kamar wuta ce mai ci har abada. Akwai wani daga cikinmu da zai iya tsira daga irin wannan wuta?”