Isaiah 37:30 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Wannan zai zama alama gare ka, ya Hezekiya, “Wannan shekara za ka ci abin da ya yi girma da kansa, shekara ta biyu kuma abin da ya tsiro daga wancan. Amma a shekara ta uku za ka yi shuki ka kuma girba, za ka dasa gonakin inabi ka kuma ci ’ya’yansu.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
سَيْ عِشَايَ يَثٜىٰ وَ سَرْكِے هٜىٰزٜىٰكِيَ، «غَا أَبِنْدَ ذَيْ ذَمَ مَكَ عَلَمَ؞ أَوَنَّنْ شٜىٰكَرَا ذَاكُثِ دَغَ أَبِنْدَ يَڟِيرَا دَ كَنْسَ؞ أَ شٜىٰكَرَا تَبِيُنْ كُمَ ذَاكُثِ أَبِنْدَ يَڟِيرَا دَغَ نَشٜىٰكَرَا تَڢَرْكُوانْ؞ عَمَّا أَ شٜىٰكَرَا تَ عُكُنْ، كُيِ نُواْمَ، كُيِ غِرْبِے، كُشُوكَ غُواْنَكِنْ إِنَبِے، كُثِ أَمْڢَانِنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Sa'an nan Ishaya ya ce wa sarki Hezekiya, “Ga alama a kan abin da zai faru. Da bana da baɗi sai gyauro za ku ci, amma a shekara ta biye za ku iya shuka hatsi ku kuma girbe shi, ku dasa kurangar inabi ku ci 'ya'yan.