Isaiah 37:38 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Wata rana, yayinda yake yin sujada a haikalin allahnsa Nisrok, ’ya’yansa maza Adrammelek da Sharezer suka kashe shi da takobi, suka kuma gudu zuwa ƙasar Ararat. Esar-Haddon ɗansa kuwa ya gāje shi a matsayin sarki.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
وَتَرَانَ يَايِنْ دَيَكٜىٰ سُجَّدَ أَطَاكِنْ غُنْكِنْسَ نِسْرُواكْ، سَيْ یَیَنْسَ مَظَا أَدْرَمّٜىٰلٜىٰكْ دَ شَرٜىٰظٜىٰرْ سُكَ كَشٜىٰشِ دَ تَكُواْبِے سُكَ غُدُ ذُوَا ڧَسَرْ أَرَرَاتْ؞ سَعَنً وَنِ طَنْسَ مَيْ سُونَ عٜىٰسَرْهَدُّوانْ يَغَاجٜىٰشِ يَذَمَ سَرْكِے؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Wata rana ya je yana sujada a gidan gunkinsa Nisrok, sai biyu daga cikin 'ya'yansa, Adrammelek da Sharezer, suka kashe shi da takubansu, sa'an nan suka tsere zuwa ƙasar Ararat. Wani daga cikin sauran 'ya'yansa, wato Esar-haddon, ya gāje shi ya zama sarki.