Isaiah 38:1 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
A kwanakin nan sai Hezekiya ya kamu da ciwo ya kuma kusa ya mutu. Annabi Ishaya ɗan Amoz ya tafi wurinsa ya kuma ce, “Ga abin da Ubangiji ya ce ka shirya gidanka, domin za ka mutu; ba za ka warke ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
عَݣُونَكِنْنَنْ هٜىٰزٜىٰكِيَ يَكَمُ دَ رَشِنْ لَاڢِيَ حَرْ يَكُسَ مُتُوَ؞ سَيْ أَنَّبِے عِشَايَ طَنْ أَمُواظْ يَذُواْ وُرِنْسَ يَثٜىٰ مَسَ «إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، ‹كَشِرْيَ غِدَنْكَ، غَمَا بَذَاكَيِ رَيْبَ، ذَاكَ مُتُ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
A lokacin nan sai sarki Hezekiya ya kamu da rashin lafiya, har ya kusa mutuwa. Sai annabi Ishaya, ɗan Amoz, ya je wurinsa domin ya gaishe shi, ya ce masa, “Ubangiji ya ce ka kintsa kome daidai, gama ba za ka warke ba. Ka yi shirin mutuwa.”