Isaiah 39:2 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Hezekiya ya marabci jakadun da murna ya kuma nuna musu abin da gidajen ajiyarsa sun ƙunsa, azurfa, zinariya, yaji, tatsatsen mai, dukan kayan yaƙinsa da kuma kome da yake a ma’ajinsa. Babu abin da yake a cikin fadansa ko cikin dukan masarautarsa da Hezekiya bai nuna musu ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
هٜىٰزٜىٰكِيَ كُوَ يَمَرَبْثٜىٰسُ؞ يَكُمَ نُونَ مُسُ طَكُنَنْ أَجِيَرْ أَرْزِڧِنْ سَرْكِے دَ أَظُرْڢَرْسَ دَ ظِينَارِيَرْسَ دَ كَايَنْ يَجِنْسَ دَ مَنْ ڧَنْشِنْسَ دَ دُكَنْ كَايَنْ يَاڧِنْسَ، وَتُواْ دُكْ أَبِنْدَ يَكٜىٰ ثِكِنْ طَكُنَنْ أَجِيَرْسَ؞ بَابُوَنِ أَبِنْدَ يَكٜىٰ ثِكِنْ غِدَنْسَ كُواْ أَبِنْدَ يَكٜىٰ ڧَرْڧَشِنْ مُلْكِنْسَ دَ بَيْ نُونَ مُسُبَ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Hezekiya kuwa ya marabci manzannin, ya kuma nunnuna musu dukiyarsa, wato azurfa da zinariya, da kayan yaji da na ƙanshi, da dukan kayayyakinsa na yaƙi. Ba abin da bai nuna musu ba a ɗakunan ajiya, da ko'ina a mulkinsa.