Isaiah 42:6 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ni Ubangiji, na kira ka cikin adalci; zan riƙe hannunka. Zan kiyaye ka in kuma sa ka zama alkawari ga mutane haske kuma ga Al’ummai,
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«نِے يَهْوٜىٰهْ ، نَا كِرَاكَ دُواْمِنْ إِنْ نُونَ أَدَلْثِنَ، ذَنْ رِڧٜىٰكَ دَ حَنُّ إِنْ صِڢَّتَاكَ، دُواْمِنْ كَذَمَ يَرْجٜىٰجٜىٰنِيَتَ غَ مُتَنٜىٰ، كَكُمَ ذَمَ حَصْكٜىٰ غَ أَلْعُمَّيْ،
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ni Ubangiji, na kira ka, na kuma ba ka iko Domin ka ga ana aikata gaskiya a duniya. Ta wurinka zan yi wa dukan mutane alkawari, Ta wurinka zan kawo haske ga al'ummai.