Isaiah 44:8 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kada ku firgita kada kuma ku ji tsoro. Ban furta wannan na kuma yi faɗar haka tuntuni ba? Ku ne shaiduna. Akwai wani Allah in ban da ni? A’a, babu wani Dutse; ban san da wani ba.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كَدَ كُجِڟُواْرُواْ، يَا مُتَنٜىٰنَ، كَدَ كُڢِرْغِتَ! تُنْدَغَ زَامَانِنْ دَا ثَنْ، بَنْ ڢَطَا نَا يِشٜىٰلَرْ أَبِنْدَ ذَيْ ڢَرُبَ؟ كُونٜىٰ شَيْدُنَ! كُواْ أَݣَويْ وَنِ اللَّهْ بَنْدَ نِے؟ بَابُوَنِ دُوڟٜىٰ، بَابُوَنِنْدَ نَسَنِ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya jama'ata, kada ku ji tsoro! Kun sani tun daga zamanin dā can, har zuwa yanzu, Na faɗa tun da wuri abin da zai faru. Ku ne kuwa shaiduna! Ko akwai wani Allah? Ko akwai wani Allah mai iko da ban taɓa jin labarinsa ba?”