Isaiah 45:13 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan tā da Sairus cikin adalcina. Zan sa dukan hanyoyinsa su miƙe. Zai sāke gina birnina ya kuma ’yantar da mutanena masu bautar talala, amma ba don wata haya ko lada ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
نِے كَيْنَ نَا تَادَ سَرْكِے سَيِرُسْ دُواْمِنْ يَثِكَ مَنُڢَاتَ مَيْ أَدَلْثِے، ذَنْ مِيڧٜىٰ دُكَنْ هَنْيُواْيِنْسَ؞ ذَيْسَاكٜىٰ غِنَا بِرْنِنَ عُرُوشَلِيمَ، يَیَنْتَرْدَ مُتَنٜىٰنَ دَسُكٜىٰ ثِكِنْ بَوْتَا، بَدُواْمِنْ عَبَاشِ لَادَ كُواْ كُطِبَ؞ نِے يَهْوٜىٰهْ مَيْ ضُنْدُنَا نَا ڢَطَا؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ni kaina na iza Sairus ya yi wani abu, Don ya cika nufina ya daidaita al'amura. Zan miƙar da kowace hanyar da zai yi tafiya a kai. Zai sāke gina birnina, wato Urushalima, Ya kuma 'yantar da mutanena da suke bautar talala. Ba wanda ya yi ijara da shi, ko ya ba shi rashawa don ya yi wannan.” Ubangiji Mai Runduna ne ya faɗi wannan.