Isaiah 45:14 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Kayayyakin Masar da hajar Kush, da waɗannan dogayen Sabenawa, za su ƙetaro zuwa wurinku za su kuma zama naku; za su bi bayanku, suna zuwa cikin sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su roƙe ku, suna cewa, ‘Tabbas Allah yana tare da ku, babu kuma wani; babu wani allah.’ ”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، «أَرْزِڧِنْ مَصَرْ دَ نَ إِتِيُواْڢِيَ ذَيْ ذَمَ نَاكُ، دُواْغَيٜىٰنْ مُتَنٜىٰنْ سٜىٰبَ ذَاسُ ذَمَ بَايِنْكُ، ذَاسُبِكُ طَوْرٜىٰ دَ سَرْڧُواْڧِ؞ ذَاسُ رُسُنَ أَغَبَنْكُ سُثٜىٰ، ‹حَڧِيڧَ، اللَّهْ يَنَ تَرٜىٰدَكُو، بَنْدَشِ، بَابُوَنِ اللَّهْ ؞› »
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ya ce wa Isra'ila, “Dukiyar Masar da ta Habasha za ta zama taku, Dogayen mutanen Seba kuma za su zama bayinku, Za su bi ku suna a ɗaure da sarƙoƙi. Za su rusuna a gabanku su tuba, su ce, ‘Allah yana tare da ku, shi kaɗai ne Allah.’ ”