Isaiah 45:18 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Gama ga abin da Ubangiji yana cewa, shi da ya halicci sammai, shi ne Allah; shi da ya sarrafa ya kuma yi duniya, ya kafa ta; bai halicce ta don ta zama ba kome ba, amma ya yi ta don a zauna a ciki, ya ce, “Ni ne Ubangiji, kuma babu wani.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
إِنْجِ يَهْوٜىٰهْ ، مَحَلِثِّنْ سَمَّيْ، اللَّهْ كَطَيْ، مَيْ صِڢَّتَا دُونِيَا، مَيْ يِنْتَ، مَيْ كَڢَتَ! بَيْ حَلِثِّ دُونِيَا تَذَمَ وُاْڢِ بَ، يَيِتَ دُواْمِنْ أَ ذَوْنَ عَثِكِنْتَ؞ شِينٜىٰ يَثٜىٰ، «نِنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ ، بَنْدَ نِے، بَابُوَنِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji ne ya halicci sammai, Shi ne wanda yake Allah! Shi ne ya shata duniya ya kuma yi ta, Ya kafa ta, ta kahu da ƙarfi, za ta yi ƙarƙo! Bai halicce ta hamada da ba kome a ciki ba, Amma wurin zaman mutane. Shi ne wanda ya ce, “Ni ne Ubangiji, Ba kuwa wani Allah, sai ni.