Isaiah 47:10 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Kin dogara a muguntarki kika kuma ce, ‘Babu wanda ya gan ni.’ Hikimarki da saninki sun ɓad da ke sa’ad da kika ce wa kanki, ‘Ni ce, kuma babu wani in ban da ni.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كِنَ يِنْ ذَمَنْكِ أَ سَكٜىٰ أَ مُغُنْتَارْكِ، حَرْ كِنَ ثٜىٰوَ ‹أَيْ، بَابُ مَيْ غَنِينَ؞› حِكِمَرْكِ دَ سَنِنْكِ سُنْ سَا كِنْ كَوْثٜىٰ دَغَ حَنْيَ، حَرْ كِنَ تُنَانِ أَ ذُوثِيَارْكِ، ‹نِے ثٜىٰ، بَنْدَ نِے، بَابُوَنِ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Kin amince da kanki cikin muguntarki, Kina tsammani ba wanda yake ganinki. Hikimarki da saninki suka sa kika ɓata, Kika kuwa ce da kanki, ‘Ni ce Allah, Ba mai kama da ni!’