Isaiah 47:8 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“To, yanzu fa, ki kasa kunne, ke mai ƙaunar nishaɗi, mai zama da rai kwance kina kuma ce wa kanki, ‘Ni ce, kuma babu wani in ban da ni. Ba zan taɓa zama gwauruwa ko in sha wahalar rashin ’ya’ya ba.’
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
«كِسَوْرَرَ كِجِ، يَا كٜىٰ مَيْ يَوَنْ سُوانْ جِنْ دَاطِے، كٜىٰ دَ كِكٜىٰ ڟَمَّنِ كِنَ ظَوْنٜىٰ لَاڢِيَ لَوْ؞ كِنَ ثٜىٰوَ أَ ذُوثِيَارْكِ، ‹نِے ثٜىٰ، بَنْدَ نِے، بَابُوَنِ، بَذَنْ ذَمَ كَمَرْ مَثٜىٰنْ دَ مِجِنْتَ يَمُتُ بَ، كُواْ مَا إِنْ رَسَ وَنِ دَغَ ثِكِنْ یَیَنَبَ؞›
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ki kasa kunne, ke mai ƙaunar nishaɗi, Ke da kike tsammani kina zaune lami lafiya. Kin ɗauka kina da girma kamar Allah, Har kina ganin ba wani kamarki. Kina tsammani ba za ki taɓa zama gwauruwa ba, Ko ki sha hasarar 'ya'yanki.