Isaiah 49:26 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Zan sa masu zaluntarki su ci naman jikinsu; za su bugu da jininsu, sai ka ce sun sha ruwan inabi. Sa’an nan dukan mutane za su sani cewa ni, Ubangiji, ni ne Mai Cetonki, Mai Fansarki, Maɗaukakin nan na Yaƙub.”
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
ذَنْسَا مَاسُ ڟَنَنْتَ مِكِ سُثِنَمً جِكِنْسُ، ذَاسُ بُغُ دَ جِنِنْسُ كَمَرْ دَ ضُوً إِنَبِے؞ سَعَنً دُكَنْ یَنْ أَدَمْ ذَيْسَنِ ثٜىٰوَ نِنٜىٰ يَهْوٜىٰهْ مَيْ ثٜىٰتُوانْكِ، نِنٜىٰ مَيْ ڢَنْسَرْكِے، مَيْ إِيكُواْ نَ يَعْڧُوبَ؞»
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Zan sa masu zaluntarku su karkashe juna, Za su yi māye, da kisankai, da fushi. Sa'an nan dukan 'yan adam za su sani, ni ne Ubangiji, Wanda ya cece ku, ya fanshe ku. Za su sani ni ne Allah Mai Iko Dukka na Isra'ila.”