Isaiah 5:25 — Compare Translations

3 translations compared side by side

Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Saboda haka fushin Ubangiji ya yi ƙuna a kan mutanensa; ya ɗaga hannunsa ya kuma buge su. Duwatsu sun jijjigu, gawawwaki kuwa suka zama kamar juji a tituna. Saboda wannan duka, fushinsa bai huce ba, bai kuwa janye hannunsa ba.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
شِيَسَا ڢُشِنْ يَهْوٜىٰهْ يَيِ ڧُونَ عَكَنْ مُتَنٜىٰنْسَ؞ يَكُمَ مِيڧَ حَنُّنْسَ يَبُغٜىٰسُ؞ مَنْيَنْ تُدَّيْ سُنْ غِرْغِظَ، غَوَوَّكِنْ مُتَنٜىٰنْ سُنْثِكَ تِيتُنَ كَمَرْ دَتِّنْ بُواْلَ؞ دُكْ دَ وَنَّنْ، ڢُشِنْ يَهْوٜىٰهْ يَڧِ يَݣُونْتَ، حَنُّنْ حُكُنْثِنْسَ يأَنَانً أَ مِيڧٜىٰ!
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ubangiji yana fushi da jama'arsa, ya miƙa hannunsa domin ya hukunta su. Duwatsu za su jijjigu, gawawwaki kuwa za a bar su a kan tituna kamar shara. Duk da haka Ubangiji ba zai huce daga fushinsa ba, ba kuwa zai janye hannunsa daga yin hukunci ba.