Isaiah 51:17 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
Ki farka, ki farka! Ki tashi, ya Urushalima, ke da kika sha daga hannun Ubangiji kwaf na fushinsa, ke da kika shanye har ƙasar kwaf kwaf da ya sa mutane suna tangaɗi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
يَا عُرُوشَلِيمَ، كِتَاشِ، كِتَاشِ! كِمِيڧٜىٰ ڟَيٜىٰ! كٜىٰ دَكِكَ شَا ݣُوڢْ نَڢُشِنْ يَهْوٜىٰهْ ، كٜىٰ دَكِكَشَا ݣُوڢْ نَحُكُنْثِ دَغَ حَنُّنْسَ، كِنْ شَنْيٜىٰشِ دُكَ، يَكُوَ سَا كِيِ تَنْغَطِ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
Ya Urushalima, ki farka! Ki tashi da kanki, ki miƙe! Kika sha ƙoƙon hukunci wanda Ubangiji, cikin fushinsa, ya ba ki ki sha, Kika shanye shi, ya kuwa sa ki yi tangaɗi!