Isaiah 51:7 — Compare Translations
3 translations compared side by side
Hausa (Sabon Rai Don Kowa 2020)
“Ku ji ni, ku da kuka san abin da yake daidai, ku mutanen da kuke da dokata a zukatanku. Kada ku ji tsoron ba’ar da mutane suke yi ko ku firgita saboda zargin da suke yi.
Hausa Arabic 2020 (أَتَّوْرَتْ دَ أَنَّبَاوَا)
كُجِنِ، كُو دَ كُكٜىٰ سَنِنْ يِنْ أَدَلْثِے، كُو مُتَنٜىٰنْ دَ كُكٜىٰ رِڧٜىٰ دَ كُواْيَرْوَاتَا أَ ذُوثِيَارْكُ! كَدَ كُجِڟُواْرُوانْ شَنْ كُنْيَا دَغَ مُتَنٜىٰ، كَدَ كُيِ ڢَرْغَبَ سَبُواْدَ ذَاغٜىٰ ذَاغٜىٰنْسُ؞
Hausa Bible 1979 (Littafi Mai Tsarki)
“Ku kasa kunne gare ni, ku da kuka san abin da yake daidai, Ku da kuke riƙe da koyarwata a zuciyarku. Kada ku ji tsoro sa'ad da mutane suke yi muku ba'a da zagi.